HomeLabaraiBa ma’aikacinmu dake karbar albashin naira miliyan 3 kowanne wata - PenCom

Ba ma’aikacinmu dake karbar albashin naira miliyan 3 kowanne wata – PenCom

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Hukumar dake kula da kudaden fanshon ‘yan Najeriya da ake kira PenCom tayi watsi da rahotan dake bayyana cewar kowanne ma’aikacin ta na karbar naira miliyan 3 kowanne wata a matsayin albashi.

Hakan dai ya biyo bayan binciken da kwamitin kudi na majalisar wakilan keyi, wanda ya bukaci bayani akan yadda Hukumar ke biyan kowanne ma’aikaci naira miliyan 2 da dubu 400 kowannne wata a matsayin albashi, kamar yadda takardun da Hukumar ta gabatar musu ya nuna.

‘Yan majalisar sun bayyana matukar bacin ransu da yadda ma’aikata a Hukumar zasu dinga karbar wadannan makudan kudade a matsayin albashi, yayin da wasu ma’aikatan da suka aje aikin su ke mutuwa ba tare da sun karbi kudaden fanshon su ba.

Shugabar Hukumar ta PenCom Aisha Dahir Umar ta kasa yiwa ‘yan majalisun gamsassun bayanai, abinda ya sa kwamitin ya baiwa Hukumar umurnin komawa domin kawo cikakkun bayanai akan albashin ma’aikata 500 dake aiki tare da ita.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories