HomeLabaraiBuhari ne ya hana saka sunan Osinbajo a kwamitin yakin neman zaben...

Buhari ne ya hana saka sunan Osinbajo a kwamitin yakin neman zaben Tinubu – APC

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Jam’iyar APC da ke mulki a Najeriya ta bayyana dalilan da suka sanya ba a sanya sunan mataimakin shugaban kasar Yemi Osinbajo a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Asiwaju Bola Tinubu ba.

A cikin wata sanarwa da kakakin tawagar yakin neman zaben Tinubu Festus Keyamo ya fitar a ranar Asabar din nan, ta ce shugaban kasar Muhammadu Buhari da kansa ne ya hana sanya sunan Osinbajo da sakataren gwamnatin kasar Boss Mustapha don su mayar da hankali a sha’anin tafiyar da gwamnati.

Rashin ganin sunan mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo a jerin sunayen mutane 422 da ke cikin kwamitin yakin neman zaben na Tinubi ya haifar da cecekuce a sassan Najeriya, ganin yadda Osinbajo ke cikin wadanda suka kalubalanci Tinubu wajen neman tikitin tsayawa jam’iyar takarar shugaban kasa.

Sai dai anga sunan tsohon ministan sifuri na kasar Rotimi Amaechi a cikin jerin sunayen, duk da cewa shi ne ya zo na biyu a zaben fidda gwanin na jam’iyyar ta APC mai mulki.

 

RFI.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories