HomeLabaraiBuhari ya karrama dan sandan da yaki karbar cin hanci a Kano

Buhari ya karrama dan sandan da yaki karbar cin hanci a Kano

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jinjinawa wani baturen ‘yan sandan kasar, SP Daniel Itse Amah dake aikin DPO a Nasarawa dake jihar Kano, saboda yadda yaki karbar cin hancin Dala dubu 200 dangane da wani bincike da yake akan fashi da makami.

Buhari ya karrama DPOn wajen taron yaki da cin hanci da rashawar da Hukumar ICPC ta shirya domin tattauna batutuwan da suka shafi cin hancvi da rashawa a tsakanin ma’aikatan gwamnati.

SP Amah ya nuna kwarewa da kuma kyamar cin hanci lokacin da ya gudanar da aikin sa na kama wani da ake kira Ali Zaki da wasu jami’an ‘yan sanda dangane da fashin kudin da ya kai naira miliyan 320.

Kafin wannan lokaci, Sufeto Janar na ‘yan sandan kasar Alkali Baba ya yawaba DPOn saboda abinda ya kira kwarewarsa da jajircewa da kuma nuna bajinta wajen gudanar da aiki.

Shugaban Hukumar ICPC Farfesa Bolaji Owasanoye ya bukaci hadin kan jama’a domin ganin an dakile ayyukan cin hanci a tsakanin al’ummar Najeriya.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories