Gwamnatin tarayya ta ba da umarnin gaggauta bude kamfanin simintin Dangote dake Obajana

0
38

Gwamnatin Najeriya ta bayar da umarnin bude kamfanin siminti na Dangote da ke Obajana a jihar Kogi.

Gwamnatin ta kuma ba da shawarar cewa dole ne a warware duk wasu batutuwan da ke cikin rikici bisa doka.

Wannan na zuwa ne kwanaki kadan fadar shugaban kasar ta shiga tsakani domin maido da zaman lafiya a kan fafutukar mallakar kamfanin siminti a Obajana tsakanin gwamnatin jihar da hamshakin attajirin Afrika, Aliko Dangote.

Rikicin dai ya sa ‘yan banga da ke aiki da umarnin gwamnatin jihar Kogi suka rufe masana’antar, bisa zargin karya haraji.

Taron da aka gudanar a misalin gwamnatin tarayya ya samu halartar shugaban rukunin Dangote, Dangote, Gwamna Yahaya Bello (Kogi) da Abdullahi Sule (Nasarawa).

A baya dai an samu rahoton cewa gwamnatin jihar Kogi ta rufe masana’antar Obajana bisa zargin kin biyan haraji da kuma mallakar sa ba a warware ba.

Sai dai mahukuntan rukunin Dangote sun ce sun kammala shirin tunkarar kotu domin neman hakkinsu kan lamarin.

Manajan Daraktan Rukunin, Dangote Cement Plc, Michel Puchercos a cikin wata sanarwa ya ce, “Muna sake jaddada cewa kamfanin simintin na Obajana mallakin Dangote Cement PLC ne 100%.

A wajen korar ma’aikatan da karfin tsiya don tabbatar da dakatarwar, ‘yan banga sun harbe ma’aikatanmu 27 tare da lalata wasu kadarorin kamfanin a masana’antar”.