HomeLabaraiNajeriya ta yi martani kan harin da aka kai wa 'yan ƙasarta...

Najeriya ta yi martani kan harin da aka kai wa ‘yan ƙasarta a Jami’ar Indiya

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Gwamnatin Najeriya ta ce ta samu rubutaccen tabbaci daga Hukumomin Indiya cewa za su kare ɗalibanta da ke can.

Shugabar Hukumar kula da harkokin ‘Yan Najeriya Mazauna Ƙetare, Abike Dabiri-Erewa ce ta bayyana haka lokacin da take mai da martani ga rahotannin cewa an kai wa ‘yan Najeriya hari a wata jami’ar ƙasar Indiya.

A ranar Litinin ne, wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda rigima ta kaure a wata harabar jami’ar da ke birnin Delhi.

Wani Farfesa a fannin binciken rikice-rikice da zaman lafiya, Ashok Swain ne yaɗa bidiyon rigimar a dandalin tiwita inda ya rubuta cewa;”Ana far wa ɗaliban Najeriya da suka zo karatu ƙasar Indiya a harabar wata Jami’a da ke kusa da birnin Delhi – ɗaliban Najeriya 30,000 ne suka biya kuɗi don yin karatu a Indiya, yayin da ‘yan Indiya 50,000 ke zaune a Najeriya suna neman kuɗi. “

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories