HomeLabaraiKu shirya wa matsananciyar yunwa a Arewa - Sarkin Zazzau

Ku shirya wa matsananciyar yunwa a Arewa – Sarkin Zazzau

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Sakamakon ambaliyar ruwan da ya addabi sassan arewacin Najeriya tare da ayyukan ‘yan bindigar da suka hana noma a yankin, Sarkin Zazzau Ahmed Nuhu Bamali ya gargadi shugabannin yankin da su tashi tsaye domin tunkarar matsalar yunwa mai tsananin dake yiwa kasar barazana.

Bamali yace mutanen yankin basa bukatar wani masanin da zai shaida musu cewar an kama hanyar karancin abincin da kuma yunwa sakamakon wadannan matsaloli guda biyu da suka hana jama’a gudanar da harkokin su na noma wanda shine babban sana’ar da aka sansu da shi.

Sarkin yace duk da yake suna ci gaba da addu’a domin Allah ya kawowa jama’a dauki, ya zama wajibi a fadakar da mutane da su tashi tsaye domin samun madogara saboda ganin girmar matsalar.

Basaraken yace lokaci yayi da jama’ar yankin zasu tashi daga baccin da suke yi domin sake dabaru ganin yadda a shekaru 2 da suka gabata, yankin yayi fama da wadanan tagwayen matsaloli a jere.

Sarkin ya kuma janyo hankalin jama’ar yankin cewar a halin da duniya take ciki a yau, babu wani yanki na duniya da ake bada ilimi kyauta, saboda haka ya dace jama’a su zage damtse wajen tallafawa bangaren ilimi, duk da yake yace baya bukatar ganin an tsawwalawa jama’a kudin makarantar.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories