Amurka ta yaba da matakan tsaro a Abuja

0
46

Gwamnatin Amurka ta yaba da kokarin da kasashen Najeriya da Afirka ta Kudu ke yi wajen tsaurara tsaro a kasashen biyu.

Hakan na zuwa ne bayan wani kashedin da Amurkan ta yi na yiwuwar afka wa Abuja, Fadar Gwamnatin Najeriya da hare-haren ta’addanci da ma wasu wurare da ke wajen birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu.

A sanarwar da Ma’aikatar Kula da Hakokin Kasashen Wajen Amurkan ta fitar, ta yaba wa kokarin da Najeriya da Afirka ta Kudun ke yi a bangaren tsaurara tsaro da nufin tunkarar duk wani hari da ya doshi manyan birnanen kasashen biyu da Amurkar ta ce ta hango.

A ranar Alhamis da ta gabata ne dai Amurkar ta yi kiran ma’aikatan jakadancinta da ke Abuja da su fice daga Najeriya, kwana guda bayan ta yi hakan ga su ma ’ya’yanta da ke a Afirka ta Kudu.

Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu, ya nuna rashin jin dadi ganin yadda Amurkar ta yi gaban kanta wajen bayyana hadarin ba tare da ta tuntubi gwamnatin kasar ba.