HomeLabarai‘Yansanda sun fatattaki ‘yan bindiga, sun ceto mutane 21 da shanu 20...

‘Yansanda sun fatattaki ‘yan bindiga, sun ceto mutane 21 da shanu 20 a Katsina

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Rundunar ‘yansandan Jihar Katsina a ranar Asabar, ta ce ta dakile harin da wasu ‘yan bindiga da suka kai inda suka ceto wasu mutane 21 da aka yi garkuwa da su tare da kwato shanu 20 da aka sace.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, SP Gambo Isah, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana cewa sun samu kiran gaggawa a ranar Asabar, kuma nan take kwamishinan ‘yansandan ya bayar da umarnin daukar matakin gaggawa yayin da jami’an rundunar suka bi sahun ‘yan bindigar a kewayen Buraji da kauyukan Sabon Sara.

A cewarsa, kwamandan yankin na Dutsinma, ACP Mohammad Makama, ya jagoranci tawagar ‘yansanda masu fikira, inda suka tare hanyar fitar kauyen Gandun Sarki, inda suka yi artabu tare da samun nasarar kubutar da duk wadanda aka yi garkuwa da su tare da kwato shanun da aka sace.

Ya ce an kashe ‘yan bindiga da dama, wasu kuma sun tsere da raunukan harbin bindiga.

Ya kuma yi kira ga mazauna jihar da su kai rahoton duk wani motsi da suka samu da kuma wadanda suka samu raunukan harbin bindiga ga ‘yan sanda domin a kama su da kuma gurfanar da su a gaban kuliya.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories