Abin da ya jawo faɗa tsakanin Murtala Garo da Ado Doguwa

0
62

Ga alama sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar APC a jihar Kano bayan da taƙaddama ta ɓarke tsakanin ƴaƴan jam’iyyar.

Yayin wani taron jam’iyyar APC a gidan mataimakin gwamnan jihar Kano a ranar Litinin, an samu hayaniyar da ta haifar da nuna yatsa tsakanin Honorabul Alhassan Ado Doguwa da kuma Murtala Sule Garo.

Sa’insa da ka-ce-na-cen ta ɓarke ne lokacin da shugaban masu rinjaye na majalisar dokokin Najeriya Honorabul Doguwa ya je gidan mataimakin gwamnan Kano a ranar Litinin.

Hon Doguwa ya shaida wa BBC cewa ko da ya isa wurin sai ya tarar ana wata ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC.

Kuma a cewarsa da ya tambayi abin da yasa ba a gayyace su ba, sai ya ce an mayar masa da kakkausar amsa.

“Tambayar kawai da na yi ita ce, ‘yanzu ya mai girma mataimakin gwamna ya kamata a ce ana taro irin wannan, ga ɓangaren gwamnati ga kwamishinoni ga ɓangaren majalisar jiha, amma mu da muke majalisar tarayya ba a gayyaci kowa daga cikinmu ba, laifin me muka yi?

“Daga faɗar hakan sai kawai yaron nan Murtala yana zaune ya ce ba za a gayyace ku ɗin ba. Waɗannan kalmomi su suka hassala ni.

“A wajen taron kuma a garin yana masifa yana zagina sai ya kifar da wani kofin shayi mai ruwa a ciki, sai santsi ya kwashe shi ya faɗi ya fasa bakinsa.

“Amma sai na ji ana ta yaɗa wani zance wan na jefe shi na ji masa rauni,” in ji Doguwa.