HomeLabaraiNDLEA ta kama makaho dan Nijar da safarar miyagun kwayoyi

NDLEA ta kama makaho dan Nijar da safarar miyagun kwayoyi

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Jami’an Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya ta sanar da kama wani mutum makaho da dansa yayin da suke kokarin safarar tabar wiwi da miyagun kwayoyi.

Cikin wani sako da NDLEA ta wallafa a shafinta na Facebook dauke da sa hannun Darektan yada labaranta, Femi Babafemi ta ce an kama mutanen biyu ne a hanyar Malumfashi Zaria a Jihar Katsina.

NDLEA ta ce mahaifin wanda shi ne makahon mai shekaru 52 da dansa mai shekaru 30, dauke da kilo 20.5 na tabar wiwi da kuma gram 10 na exol-5.

NDLEA ta bayyana cewa asalin mutanen sun fito ne daga Jihar Damagaram da ke Jamhuriyar Nijar.

Kazalika, NDLEA ta ce jami’anta na sintiri ne suka cafke mutanen a hanyarsu ta komawa Nijar.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories