HomeLabarai‘Yan sanda sun kwato shanu 500 da babura 8 a Neja

‘Yan sanda sun kwato shanu 500 da babura 8 a Neja

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Rundunar ‘yansandan Jihar Neja ta kwato shanu akalla 500 da babura takwas da ‘yan bindiga suka kwace a yayin wata musayar wuta da suka yi daga wasu kananan hukumomi uku na jihar.

Kananan hukumomin sun hada da Paikoro, Munya da Wushishi.

Rundunar, a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Wasiu Abiodun, ya sanya wa hannu, ta ce jami’an rundunar sun samu nasarar dakile dukkanin hare-haren.

Ya ce a ranar Laraba wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai farmaki kauyen Kaffin-Koro da ke karamar hukumar Paikoro, ta kauyen Adunu, inda suka rika harbe-harbe ba tare da bata lokaci ba, kuma a cikin haka ne wasu mutane biyu suka samu raunuka harsashi yayin da aka yi awon gaba da wasu shanu.

‘Yan bindigar sun yi watsi da shanun da aka sace, yayin da aka kai wadanda suka jikkata zuwa asibitin Janar na Kaffin-Koro kuma suna karbar magani”.

 A cewar rundunar ‘yansandan a ranar Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka yi awon gaba da wasu shanu da ba a tantance adadinsu ba daga garuruwan Akare, Jiwawa, Gulanji, Kadaura, da wasu kauyuka da ke makwabtaka da Wushishi suna kokarin tsallakawa hanyar Tegina zuwa Zungeru tsakanin kauyukan Garun-Gabas da Yakila.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Rundunar ‘yansanda d sojoji sun hada kai tare da mayar da martani cikin gaggawa inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.

“Sakamakon haka ‘yan bindigar sun yi watsi da shanun da suka sace da wasu babura a yayin da suka shiga cikin rudani domin tsira da raunukan harbin bindiga a dajin.

Abiodun ya kara da cewa, a ranar Litinin din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari kauyen Chibani ta gundumar Kuchi ta karamar hukumar Munya, yayin da jami’an ‘yansanda da jami’an ‘yan banga suka tattaru zuwa yankin inda suka yi artabu da ‘yan bindigar.

Ya kara da cewa, “An samu nasarar fatattakar ‘yan bindigar, inda suka yi watsi da shanun, yayin da suka tsere ta Kauyen Rishi Kaduna.

Sai dai wasu mutane biyu daga cikin ‘yan banga na yankin sun rasa rayukansu a yayin artabu da bindiga.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories