HomeLabaraiIlimiGanduje ya ware naira miliyan 300 zai biya kudin karatun daliban...

Ganduje ya ware naira miliyan 300 zai biya kudin karatun daliban Kano da ke karatu a waje

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Gwamnan jihar Kano, Dakta Umar Ganduje, ya amince da sakin Naira miliyan 300 a matsayin kudin karatu ga dalibai ‘Yan asalin jihar Kano da gwamnati ta dauki nauyin karatu a jami’ar Near East University, Cyprus.

Kwamishiniyar ilimi mai zurfi, Dokta Mariya Mahmoud Bunkure, ta bayyana hakan.

Dokta Bunkure ta ce biyan kudin makarantar yana cika alkawarin da Gwamna Ganduje ya yi musanman saboda daukaka martabar zamantakewa da tattalin arzikin matasan jihar ta hanyar samar da ingantaccen ilimi a kan lokaci.

Kwamishinan ta gode wa gwamnan da ya tabbatar da mafarkinta.

Ta taya daliban da iyayensu murnar samun irin wannan gagarumin tallafi tare da bukatarsu da su yi kyakkyawan amfani da ilimin da suka samu wajen ci gaban jihar Kano da ma Nijeriya baki daya.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories