HomeLabaraiIlimiSadique Abubakar ya bai wa dalibai 201 tallafin karatu a Bauchi

Sadique Abubakar ya bai wa dalibai 201 tallafin karatu a Bauchi

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...
Dan takarar gwamnan jam’iyyar APC a Jihar Bauchi, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (mai ritaya), ya bai wa dalibai 201 tallafin karatu a Kwalejin Kiwon Lafiya da ke jihar.

Da yake jawabi yayin gabatar da tallafin karatu ga daliban da suka amfana a ranar Litinin a harabar kwalejin, Sadique Abubakar, ya shawarci daliban da su rika daukar karatunsu da muhimmanci ta yadda za su yi fice kuma su zama masu amfani ga al’umma.

Ya ce “Ilimin kiwon lafiya na da matukar muhimmanci ga rayuwar al’umma, don haka ku dauki karatunku da muhimmanci.”

Abubakar ya caccaki gwamnatin mai ci kan yadda ta ki bai wa fannin ilimi kulawa, inda ya kara da cewa idan aka zabe shi zai ci gaba da tallafa wa marasa galihu da marasa karfi a cikin al’umma domin samun ilimi mai inganci.

Abubakar ya kuma nuna bacin ransa ga gwamnati mai ci kan watsi da yarjejeniyar tallafin ilimi da gwamnatin da ta shude ta yi.

A cewarsa, “Abun bai dace ba, ilimi ba abu ne da gwamnati ita kadai ba za ta iya ba. Idan aka zabe mu, zamu sake duba batun ta yadda za a sake duba yarjejeniyar ilimi.”

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories