HomeLabaraiBayan sake fasalin Naira, Dala na iya karye wa zuwa N200, in...

Bayan sake fasalin Naira, Dala na iya karye wa zuwa N200, in ji shugaban EFCC

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin-hanci da Rashawa ,EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya ce dala za ta iya faɗuwa zuwa naira 200 bayan sake fasalin Naira.

Bawa ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da Sashen Hausa na Deutsche Welle (DW), wanda Daily Trust ta saurara, inda ya ce shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi abu mai kyau wajen amince wa da sake fasalin kuɗin.

Ya ce, “Doka ta ce za a sake fasalin takardar kudin Naira duk bayan shekara takwas amma mun shafe shekaru 20 ba tare da wani canji a kansu ba.

“Kuma hakan ya sanya kashi 85 cikin 100 na kudaden ke yawo ba a bankuna ba, a lokacin da CBN ya zo da wannan gyara, dala ta koma 880 daga baya ta koma 680 ko kusan haka.

“Don haka ka ga da wannan sake fasalin ma Naira, dala na iya faduwa sosai, wa ya sani ma ko ta kai ₦200.”

Shugaban hukumar ta EFCC ya kuma ce babu wata manufa ta siyasa a bayan wannan manufar, inda ya kuma yi kira ga ƴan Nijeriya da su kai rahoton duk wanda ya ɓoye kudade.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories