HomeLabaraiZa mu cire tallafin man fetur a 2023 - Gwamnatin tarayya

Za mu cire tallafin man fetur a 2023 – Gwamnatin tarayya

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...

Ministar kudi, kasafi da tsare-tsare, Zainab Ahmed, ta bayyana cewar gwamnatin tarayya za ta daina biyan kudin tallafin man fetur a watan Yunin 2023.

Zainab, ta bayyana haka ne a lokacin da ta gana da manema labarai a Abuja, babban birnin tarayya bayan kammala taron tattalin arziki na kasa karo na 28.

Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), ya rawaito cewa biyan tallafin kudin man fetur ya lashe Naira tiriliyan 2.565 tsakanin watan Janairu zuwa Agustan 2022.

Har wa yau, kuma a cikin kasafin kudin bana, gwamnatin tarayya ta kiyasta za ta kashe Naira tiriliyan 3.3 wajen biyan tallafin man fetur din tsakanin watan Janairu zuwa Yunin 2023.

Ta kara da cewa kudin tallafin man fetur din na kawo wa kasafin kudin gibin da dole sai an ciwo bashi kafin cike shi.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories