HomeLabaraiAn kama wani likitan bogi a Neja

An kama wani likitan bogi a Neja

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta samu nasarar kama wani mutum mai suna Clement Joseph da ke garin Koropka, karamar hukumar Chanchaga, wanda yake bayyana kansa a matsayin likita.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar DSP Wasiu Abiodun, ya sanar da manema labarai a garin Minna.

Ya ce, sun kama likitan bogin kan wasu laifuka guda uku da ake zarginsa da aikata wa.

Ya ce, “An kama wanda ake zargin da laifin yin karyar cewa, shi likita ne ya kuma karbi kudi a hannun wani mutum da sunan zai yi masa magani”.

Abiodun ya ce, kokacin da ake yi masa tambayoyi, ya tabbatar da cewa, shi ba likita ba ne.

 A karshe dai, za a ci gaba da bincike domin tabbatar da gaskiyar abin da ya faru, wanda kuma idan laifin da ake zarginsa da shi ya tabbata zai gurfana gaban kitu, domin yi masa gukunci.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories