HomeLabaraiTurji ya tsare yan aike bayan sun kai masa harajin N10m

Turji ya tsare yan aike bayan sun kai masa harajin N10m

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Dan ta’addan nan da ya addabi yankin Zamfara da Sakkwato, Bello Turji, ya yi garkuwa da ’yan aike da suka je kai mishi Naira miliyan 10 da ya sanya wa garinsu haraji.

A ranar Talata ne Turji ya sa yaransa su yi awon gaba da biyar daga cikin mutum bakwai da suka kai mishi kudin a matsayin ‘harajin kariya,’ da ya sanya wa garin Moriki da ke Karamar Hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara.

Wani dan garin, Sani Moriki ya ce, “Da aka shida wa Turji cewa Naira miliyan 10.5 ne kudin da aka kai ba miliyan N2o da ya bukata ba sai ya fusata, ya umarci yaransa su rike biyar daga cikin ’yan sakon su tafi da su Dajin Jirari; ko da yake biyu daga cikin mutanen sun dawo gida yau da safe.”

Sani ya ce, “Yanzu muna cikin tashin hankali kuma muna kokarin tuntubar sa kan yadda za mu kai masa cikon Naira miliyan 10 din. Al’ummarmu na cikin tsananin tashin hankali.

 

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories