HomeLabarai'Yan bindiga sun sace fiye da mutum 100 a Zamfara

‘Yan bindiga sun sace fiye da mutum 100 a Zamfara

Date:

Related stories

INEC ta ce ba a kammala zabe a jihar Adamawa ba

Hukumar zaben Najeriya INEC, ta ayyana zaben gwamnan jihar...

An kashe ‘yan sanda 2, da dama sun raunata a wata arangama da sojoji a Taraba

A ranar Litin ne wasu sojoji suka kashe ‘yansanda...

Gwamna Zulum ya sake lashe zaben gwamna a jihar Borno

Sakamakon da hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar...

Sojoji sun kashe hatsabinin dan ta’adda Umaru Nagona

Dakarun sojin Najeriya sun hallaka, Umaru Nagona, daya daga...

An kona gidan mawakin siyasa Rarara a Kano

Wasu da ake zargi ’yan daba ne sun banka...
Sama da mutane 100 ne aka tabbatar da cewa wasu ’yan bindiga sun yi garkuwa da su a Jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Gidan Rediyon Jamus DW ya ruwaito cewa, wasu dauke da bindigogi sun shiga kauyuka hudu na Jihar Zamfara, inda suka kwashi mutanen da suka hada da mata da kuma kananan yara.

Fiye da mutum 40 aka kwashe daga kauyen Kanwa na Karamar Hukumar Zurmi, yayin da wasu 37 din su ma aka kwashe su daga kauyen Kwabre, a cewar Kwamishinan Watsa Labarai na Jihar Zamfara, Malam Ibrahim Dosara.

Haka ma a cewar Malam Dosara, an kwashi wasu mutane akalla 38 a kauyukan ’Yankaba da Gidan-Goga da ke Karamar Hukumar Maradun.

Garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a Arewacin Najeriya dai, ta zama wata gagarumar matsalar da ke faruwa ba dare da rana, kama daga cikin gonaki zuwa kan hanyoyi na manyan da kananan garuruwa.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories