HomeLabarai'Yan Majalisa sun bai wa hammata iska a Saliyo

‘Yan Majalisa sun bai wa hammata iska a Saliyo

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Sabani a kan wata sabuwar dokar zabe a Saliyo ya haddasa fada a tsakanin ‘yan majalisar dokokin kasar, inda suka rika bai wa hammata iska a zauren majalisar.

Abin da masu amfani da shafin twitter ‘yan saliyo suka kira hatsaniya an ga yadda ake ta kutufar juna a zauren majalisar.

An rika wurgi da sandar iko ta majalisar daga nan zuwa can.

Wani dan jarida ya ce daga nan ne kuma sai jami’an tsaro suka shiga tsakani inda suka yi waje da wasu daga cikin ‘yan majalisar.

BBC Hausa ta ce rikicin ya barke ne tsakanin ‘yan majalisar jam’iyya mai mulki da kuma na jam’iyyun hamayya a kan wani kuduri na sanya wakilci a hukumar zaben kasar daidai da karfin kowace jam’iyya a kan shirin zabukan da za a yi a shekara mai zuwa.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories