HomeLabaraiSiyasaBabu wanda zai samu kuri'u miliyan 1.9 da Buhari ya samu a...

Babu wanda zai samu kuri’u miliyan 1.9 da Buhari ya samu a Kano a 2015 – Datti Ahmed

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Datti Baba-Ahmed, ya ce sama da kuri’u miliyan 1.9 da shugaban kasa, Manjo Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya) ya samu a jihar Kano a zaben 2015, ba dan takara zai samu wannan kuri’u a zabe mai zuwa.

A shekarar 2015, Buhari na jam’iyyar All Progressives Congress, ya doke jam’iyyar PDP ta Goodluck Jonathan da kuri’u 1,903,999, yayin da shi kuma ya samu kuri’u 215,779 a Kano.

“Kuri’un arewacin Najeriya da suke jiran a samu rarrabuwar kawuna wanda ko wanne daga cikin biyun da suka zo na biyu ke fatan samu, ya zama ba su samu ba,” in ji Baba-Ahmed a yayin wani shiri kai tsaye a gidan talabijin na Channels. Shirin zabe na musamman na Talabijin Hukuncin 2023 a ranar Talata.

“Masu kaikayi – misali Kano – yanzu ba kamar 2015 ba ce na yadda kuri’arta a  shekarar 2015, kuri’u miliyan 1.9 na Kano, babu wanda zai yi kwadayin samunta ko shakka babu sai Buhari in da ya yiwa Jonathan wanwar. Babu wanda zai samu haka a Kano a 2023.”

Baba-Ahmed ya ce sauran shiyyoyin da ake fafatawa a Arewa sune Kaduna da Katsina.

Kamar yadda gidan Talabijin din Channels ya ruwaito, wasu abubuwan da ya yi imanin suna taimaka wa jam’iyyarsa sun hada da bunkasar matasa a jiharsa ta Kaduna, da kara wayar da kan jama’a kan hada kan Najeriya, da kuma wadanda’yan asalin yankin  Kaduna ta kudu ne .

“Muna da jama’a mai yawa fiye da sanin abokan takarar mu,” in ji shi.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here