HomeLabaraiYadda ’yan Boko Haram da ISWAP suka kashe juna a Borno

Yadda ’yan Boko Haram da ISWAP suka kashe juna a Borno

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Mayakan Boko Haram da na ISWAP sun hallaka juna a wata arangama tsakanin kungiyoyin ’yan ta’addan domin kwace iko a yankin Arewa maso Gabas da Tafkin Chadi.

’Yan ta’adda da dama kuma sun samu raununka a artabun da suka yi a kauyukan Nguro da Ngoldiri da ke yankin Timbuktu Triangle a Damboa, Jihar Borno.

Arangama ta wakana ne da misalin karfe 12 na dare a daidai lokacin da kungiyar ISWAP ta kai hari kan wasu mayakan Boko Haram da ke tafiya.

Rikicin baya-bayan nan na ranar 7 ga watan Fabrairun 2023 a Timbuktu wanda ya dauki tsawon awanni 3 ana yi, ya yi sanadin mutuwar mayaka da dama daga kungiyoyin ta’addan.

Yayin da ake kara samun hare-hare tsakanin ISWAP da Boko Haram, an gano cewar ISWAP na shirin kaddamar da wasu hare-hare a yankin Dajin Sambisa, Marte da Abadam don kwato wasu yankuna daga Boko Haram.

A gefe guda kuma Boko Haram na yin tattaki a Dajin Sambisa da tsaunin Mandara domin fuskantar ’yan ta’addar ISWAP.

Don sake farfado da karfinta na yaki, Boko Haram ta nada wani Alhaji Ali Hajja Fusam, dan asalin Bama a matsayin sabon shugabanta a Gaizuwa, sansanin da sojojin Operation Hadin Kai suka sha lalatawa.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here