Messi, Mbappé da Benzema a zagayen karshe na cin kofin Fifa na zakaran dan wasa

0
84

Dan wasan Argentina Lionel Messi da Kylian Mbappé na Faransa da Karim Benzema su ne ‘yan wasa uku da suka fafata a gasar Fifa na gwarzon dan wasan bana, in ji Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya a yay Juma’a.

Bangaren mata, ‘yar kasar Spain, Alexia Putellas, wadda ke rike da kambun gasar, za ta fafata da ‘yar wasan Ingila Beth Mead da ‘yar Amurka Alexis Morgan.

Bayan sun kara da juna a wasan karshe na gasar cin kofin duniya, Messi da Mbappé, da ke taka leda  Paris Saint-Germain, suna fafatawa don maye gurbin Robert Lewandowski dan kasar Poland, wanda aka lashe a shekarar 2020 da 2021, tare da Benzema, wanda ya lashe gasar Ligue karo na biyar tare da. Real Madrid. Za a sanar da wadanda suka yi nasara a ranar 27 ga watan Fabrairu a Zurich, hedkwatar hukumar ta Fifa.

Bangaren masu horar da kungiyoyi ,wanda ya lashe kofin duniya Lionel Scaloni (Argentina) da Pep Guardiola (Manchester City) da kuma wanda ya lashe gasar zakarun Turai tare da Real Madrid, Carlo Ancelotti zasu fafata da nufin lashe wannan kyauta.

Kungiyar ta kasa da kasa za ta bayar da kyauta ga koci, mai tsaron gida , sannan kuma ta shirya gasar cin kofin magoya bayanta da lambar yabo ta Puskas na gwarzon shekara, wanda Dimitri Payet (Marseille-PAOK Salonika) da Richarlison (Brazil-Serbia) suke layin wandada ake sa ran zasu iya lashe wannan kyautar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here