HomeLabaraiSiyasaJami'an tsaro sun kama masu bangar siyasa kusan 100

Jami’an tsaro sun kama masu bangar siyasa kusan 100

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta sanar da kama matasa 93 bisa zargin su da bangar siyasa da tayar da zaune tsaye yayin da jam‘iyyu ke tarukan yakin neman zabe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mamman Dauda ne ya tabbatar da kamen matasan ta cikin wata sanarwa da ya fitar mai dauke da sa hannun kakakain rundunar ‚yan sanda Abdullahi Haruna Kiyawa.

Kwamishinan ‘yan sandan ta cikin sanarwar yace an kama matasan ne bisa umarnin babban sufeton ‘yan sandan kasar Usman Alkali baba na kakkabe dukannin matasan da ke ikirarin daba a kasar baki daya.

A cewar sa an kama matasa ne a wani samame da ‘yan sandan suka kai filin taro na Sani Abacha da ke jihar lokacin da wata jam’iyya ke taron yakin neman zaben ta.

A cewar sa an kama matsan da bindigogi kirar gargajiya guda biyu, da wukake guda 32 da adda guda 1 sai kuma layoyi da guru masu tarin yawa.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here