HomeLabaraiBadakalar kudade: Za a ci gaba da sauraran karar da EFCC ta...

Badakalar kudade: Za a ci gaba da sauraran karar da EFCC ta shigar da matar gwamnan Kogi

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

A ranar Litinin 13 ga Fabrairu, 2023 za a ci gaba da sauraron karar da aka shigar da dan dan uwan Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, Ali Bello da matarsa Rashida Bello kan badakalar karkatar da kudade a gaban Mai Shari’a Obiora Egwuatu na Babban Kotun Tarayya dake Abuja.

Ali Bello na daga cikin mutane hudu da aka kama a ranar 8 ga Fabrairu, 2023 kan tuhume-tuhume 18 da suka hada da almubazzaranci da kudade har naira Biliyan N3,081,804,654.00.

Sauran wadanda ake tuhumar su ne Abba Adauda, Yakubu Siyaka Adabenege da kuma Iyada Sadat.

Wadanda ake tuhumar dai, sun ki amsa laifin da ake tuhumarsu da su.

Dangane da kin amsa laifin da ake tuhumarsu da shi, lauya mai shigar da kara, Rotimi Oyedepo, ya bukaci kotun da ta kara musu wani lokaci domin gabatar da cikakkiyar hujja kan tuhume-tuhumen.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here