HomeLabaraiINEC ta fitar da jerin rumfunan zabe 124 da ta soke

INEC ta fitar da jerin rumfunan zabe 124 da ta soke

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Kwana 10 kafin zaben shugaban kasa,  Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta fitar da jerin sunayen rumfunan zabe 124 da ta soke.

INEC ta ce ta soke rumfunan zaben ne a wasu jihohi 15, saboda babu ko mutum daya da ke da rajista a cikinsu, don haka, ba za a yi zabe a nan ba a wannan karon.

Jerin sunayen rusassun rumfunan zaben da INEC ta fitar ya nuna Jihar Imo ce a kan gaba da rumfunan zabe 38 da ka soke.

Ga jerin jihohin da abin ya shafa da kuma yawan rumfunan zabensu da INEC ta soke:

  1. Imo – 38
  2. Abia – 12
  3. Borno – 12
  4. Binuwai – 10
  5. Kano – 10
  6. Kaduna – 8
  7. Anambra – 6
  8. Bauchi – 6
  9. Adamawa – 4
  10. Delta – 4
  11. Ebonyi – 4
  12. Enugu – 4
  13. Jigawa – 3
  14. Bayelsa – 2
  15. Edo – 1.

A ranar 25 ga watan Fabrairu da muke ciki ne dai za a gudanar da zaben shugaban kasa na da Majalisun Tarayya, wanda bayansa da mako biyu za a gudanar da na gwamnoni da Majalisun jihohi a ranar 11 ga watan Maris, 2023.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here