HomeLabaraiAn mayar da kwalejin Sa’adatu Rimi da ke Kano matsayin jami’a

An mayar da kwalejin Sa’adatu Rimi da ke Kano matsayin jami’a

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Gwamnatin Tarayya ta sahale wa Jihar Kano ta daga likafar Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso a zuwa matsayin jami’ar Jiha.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Jami‘o’i ta Kasa (NUC), Farfesa Abubakar Rasheed ne ya bayyana hakan lokacin da yake gabatar da takardar shaidar ga Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje.

Rasheed ya ce Jami’ar za ta taimaka wajen kara habaka bangaren ilimi a jihar, la’akari da takardun shaidar tsare-tsaren jami’ar da gwamnatin jihar ta gabatar wa NUC.

“Bisa cika ka’idojin zamowa jami’a da kwalejin ta yi, a madadin hukumar NUC, ina farin cikin sanar da ku cewa, daga ranar Talata, 14 ga watan Fabrairun 2023, ta tashi daga Kwalejin Ilimi ta koma Jami‘ar Jiha ta 61, kuma ta 221 a jami’o’in Najeriya baki daya,” in ji Farfesa Rasheed.

Ya kuma ce Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Jami’a (JAMB), da Asusun Tallafawa Jami’o’i (TETFUND), da ta Hukumar Kula da Matasa Masu yi wa Kasa Hidima (NYSC) sun samu ta su sanarwar a hukumance.

A nasa bangaren Gwamna Ganduje cewa ya yi jami’ar za ta fara aiki da fiye da lakcarori 116 da ke da takardun shaida matakin karatu na digiri na uku (PhD), da kuma guda 246 da ke matakin digiri na biyu (Masters).

“Baya ga haka kuma, shirye-shirye sun yi nisa na ganin an tsara kammala karatun daliban da ke yanzu haka ke karatu a ciki tana kwaleji, kafin zamowarta jami’a” in ji Gwamnan.

Ya kuma ce yunkurin na sa dori ne kan tsohon Gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso ya fara, na samar wa jihar jami’o’i har biyu.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here