Matashi ya tsere ya bar budurwasa da kwayenta bayan sun ci abincin sama da 200,000

0
71

Matashin Bakano ya bada labarin yadda budurwarsa ta kwashi kawayenta 3 suka nemi firgita tattalin arzikinsa ta hanyar cin abincin N220,000 a Gusto.

Matashin mai suna Abdul ya bayyana cewa, abincin dubu takwas kacal ya nema amma a karon farko sun bukaci abincin N155,000.

Zatonsa haka za a tsaya, sun zage tare da bukatar a kwai musu abincin Turai da na gida Najeriya har suka kai N220,000

Ganin hakan ya rikita shi yace zai dauko katin bankinsa a mota inda daga fitarsa ya samu kira daga gida kuma yayi amfani da damar ya cika bujensa da iska.

Abdul ya bada cikakken yadda abun ya faru a shafinsa na twitter

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here