HomeLabaraiNa bai wa bankuna umarnin wadata mutane da takardun N200 – Emefiele

Na bai wa bankuna umarnin wadata mutane da takardun N200 – Emefiele

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya bayyana cewa ya gana da shugabannin bankunan kasuwanci 15 inda ya ba su umarnin wadata mutane da takardun Naira 200.

A cewarsa, ya tattauna da su yadda za a sassauta karancin kudi da ake fama da shi a kasar nan, biyo bayan umarnin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayar a safiyar ranar Alhamis.

Buhari ya ba da umarnin a sake dawo da tsoffin takardun kudi na N200 don ci gaba da amfani da su har zuwa ranar 10 ga Afrilu.

Emefiele ya zanta da manema labarai na fadar shugaban kasa jim kadan bayan halartar taron da Buhari ya yi da kwamitin majalisar wakilai a fadar shugaban kasa inda sabon tsarin musanya naira.

Emefiele ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa za a samar da tsofaffin takardun kudi na N200 nan take.

A safiyar ranar Alhamis ne shugaba Buhari ya bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudin duk da umarnin da kotun koli ta bayar.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here