Gobarar Maiduguri: Zulum ya ba wa ’Yan kasuwa tallafin Naira biliyan 1

0
94

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ya karbi bakuncin daruruwan ’yan kasuwar Monday Market, wadanda iftila’in gobara ya shafa.

Yawancin ’yan kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Maiduguri, babban birnin jihar, sun rasa shagunansu da kayayyakinsu na biliyoyin Naira a gobarar da ta tashi da gabanin wayewar garin ranar Lahadi.

A lokacin da ya karbi bakuncinsu, Zulum ya ya mika musu cekin kudi na Naira biliyan daya su raba a matsayin agajin gaggawa ga wadanda abin ya shafa, har zuwa lokacin da kwamitin bincike zai fitar da sakamakon aikin da aka sa shi.

A cikin  jawabinsa ga al’ummar jihar a ranar Lahadi bayan ziyarar gani da ido a kasuwar, Gwamna Zulum  ya  yi alkawarin tallafin Naira biliyan daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here