Sabon zababben shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya ce ya shirya tsaf domin tunkarar duk wani sammaci daga dan takarar Jamâiyyar PDP, Atiku Abubakar, zai yi masa.
A wani taron manema labarai a ranar Alhamis, Atiku ya ce zaben na ranar Asabar da ta gabata wanda Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), ta sanar cewa Tinubu ya lashe, a matsayin zabe mara inganci.
Sai dai a wani martani da ya mayar da Festus Keyamo (SAN) ya fitar, Tinubu ya ce, âShirin Atiku Abubakar na kalubalantar sakamakon zaben abin farin ciki ne.
âMun shirya don tunkarar kalubalensa, kowane iri a koâina sannan a koyaushe.
Idan Atiku Abubakar ba zai iya goya wa zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu baya ba, abin da ya fi masa shi ne sali-alin ya koma Dubai da zama.
âAtiku Abubakar ya yi murna bai zo na uku ko na hudu a zaben ba, saboda da sai ya fi fuskantar tozarci.
âNa farko, Atiku Abubakar ya karya kaâidar shiyya-shiyya a cikin jamâiyyarsa ta hanyar dagewa sai ya tsaya takarar shugaban kasa.
âBayan fitowa takara, ita kanta PDP ta ci gaba da yi wa shugabannin Kudancin jamâiyyar zagon kasa, ta hanyar bai wa Atiku takara.
âWannan ba shakka ya haifar da tawaye daga gwamnonin G-5 tare da yi wa PDP zagon kasa kafin zabe da kuma a rumfunan zabe.
âRashin hada kan jamâiyyarsa shi ne dalilin da ya sa ya fadi zabe,â in ji Festus Keyamo.
Atiku dai kamar abokin hamayyarsa na jamâiyyar LP, Peter Obi ya ce ya shirya zuwa kotu don kalubalantar nasara Tinubu a zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu.