Jaridar Najeriya ta bukaci gurfanar da gwamnan CBN gaban kotu

0
60

Babbar kafar yada labarai ta Najeriya, Premium Times ta yi kira da a kama Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin kasar tare da gurfanar da shi gaban kuliya.

A bugun ta na yau asabar, PREMIUM TIMES ta sake jaddada matsayin ta, inda ta nuna rashin jin dadi kan manufofin cin hanci da rashawa da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sanya a karkashin shugabancin Emefiele.

Editan PREMIUM TIMES  ya kuma caccaki CBN kan kin bin hukuncin da kotun koli ta yanke kan tsofaffin takardun kudin Naira. An yi nuni da cewa, dokar cire tsabar kudi da babban bankin ya sanya, cin zarafi ne ga ‘yancin dan Adam.

Kwanaki kadan gabanin babban zaben kasar da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tabbatar da manufar musanya naira da babban bankin kasar CBN ya tsara wanda ya sabawa hukuncin kotun. Shugaba Buhari ya roki ‘yan Najeriya da su jajirce duk da irin wahalhalun da gwamnatinsa ke fuskanta.

Gwamnatocin Kaduna, Kogi, da Zamfara sun shigar da karar gwamnatin tarayya a gaban kotun koli, inda suke neman a ba su umarnin soke yunkurin da babban bankin Najeriya CBN ya yi a baya-bayan nan na yin tsaffin takardun kudi na N200, N500 da N1000.

Sai dai kuma gwamnatin tarayya da na CBN ba su yi wani yunkuri a hukumance na aiwatar da umarnin kotun koli ba, duk da fushin jama’a.

Sai dai PREMIUM TIMES na neman a kama Shugaban babban bankin Najeriya Godwin Emefiele tare da gurfanar da shi gaban kuliya bisa rashin biyayya ga kotu da kuma take hakkokin ‘yan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here