Dapo Abiodun na jam’iyyar APC ya yi tazarce a Ogun

0
38

Gwamnan jihar Ogun Dapo Abiodun ya samu nasara a zaɓen gwamnan jihar da da aka yi a ranar Asabar.

Babban jami’in zaɓen na jihar, Farfesa Kayode Adebowale ne ya bayyana sakamakon da yammacin Lahadi.

Abiodun ya lashe zaben da ƙuri’u 276,298, inda ya samu nasara a kan abokin hamayyarsa Ladi Adebutu na jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’u 262,383, sai kuma Biyi Otegeye na jam’iyyar ADC da yazo na uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here