Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

0
50

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar hukumar Kura a jihar Kano ya yanke jiki Ya fadi a kofar hedikwatar INEC ta Kano, yanzu haka yana kwance a wani asibiti da ba a bayyana ba.

Abokin aikinsa na karamar hukumar Garun Malam, Muhammad Shuaibu Abubakar da suka zo a mota daya da shi, zai gabatar da sakamakon zaben a madadinsa, jami’ar zabe, Maryam Adamu Abdullahi ta karamar hukumar Kura za ta taimaka masa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here