Mutum 21 aka kashe a tashin hankalin bayan zaɓen gwamnoni – EU

0
42

Tawagar Ƙungiyar Tarayyar Turai da ta sa ido a zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisar jihohi na ranar 18 ga watan Maris ta ce an kashe kimanin mutum 21 sakamakon tashin hankalin da aka samu a wasu jihohin Najeriya.

EU ta bayyana haka ne yayin da ake ci gaba da sanar da sakamakon zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisar dokokin wasu jihohin.

Babban jami’in da ya sanya ido a zaɓen na Najeriya, Mista Barry Andrews ne ya bayyana wa ƴan jarida hakan ranar Litinin game da sakamakon bincikensu da suka yi game da zaɓen.

Barry ya ƙara da cewa mutane da dama ba su fita kaɗa ƙuri’a ba galibi a cewarsa saboda rashin biyan buƙatun masu zaɓe a zaɓen shugaban ƙasar da ya gudana.

Tawagar masu sa idon ta EU ta kuma ce an samu matsalolin da suka shafi sayen ƙuri’u a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya kuma yaba wa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya INEC saboda yadda ta gyara wasu kura-kuran da aka fuskanta a yayin zaɓen shugaban ƙasa musamman ta fuskar jigilar kayayyakin zaɓe.

Mista Barry ya kuma ce INEC ta inganta tsarin zaɓn ta hanyar aikewa da kuma amfani da na’urorin tantance masu zaɓe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here