Ba za mu janye sababbin kuɗi daga hannun mutane ba – CBN

0
70

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya musanta raɗe-raɗin da ke cewa bankin na ƙoƙarin yanke shawarar janye sababbin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da 1,000.

A wata sanarwa da bankin ya fitar ta hannun mai riƙon muƙamin daraktan yaɗa labarunsa, AbdulMumin Isa, bankin ya bayyana raɗe-raɗin a matsayin ‘maras tushe.’

Bankin ya ce a halin yanzu za a ci gaba da amfani da tsofaffi da sababbin kuɗaɗen kamar yadda suke.

Haka nan ya ƙara da cewa bankin na ci gaba da karɓar takardun sababbin kuɗaɗen daga kamfanin buga takardun kuɗi na ƙasar.

Ya ce kamar yadda aka sanar a baya za a ci gaba da amfani da kuɗin har zuwa 31 ga watan Disamba, lokacin da za a janye su daga hannun al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here