Wani hatsarin jirgin kasa ya kashe kusan mutum 30

0
89

Akalla mutane 28 ne suka mutu, sama da 300 kuma suka jikkata, kana ana fargabar da dama sun makale a wani hatsarin jirgin kasa da ya afku a jihar Odisha da ke gabashin Indiya.

Hukumomin kasar sun shaidawa kafafen yada labarai na cikin gida cewa jirgin fasinja na Coromandel Express da wani jirgin kaya sun yi karo a kusa da Balasore mai tazarar kilomita 200 daga Bhubaneswar babban birnin jihar.

Wani jirgin fasinja na biyu shi ma ya shiga cikin lamarin, a cewar babban sakatare na Odisha Pradeep Jena, amma har yanzu ba a fayyace yadda lamarin ya kasance ba.

Jaridar Trust ta Indiya ta ce, kimanin mutane 50 ne ake fargabar sun mutu, a cewar, kuma akwai fasinjoji da yawa da suka makale a karkashin jiragen.

Wani jami’in ‘dan sanda a Balasore ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa da yawa daga cikin wadanda suka jikkata na cikin wani mawuyacin hali, sai dai har yanzu ba a bayyana cikakken bayani ba.

Kafofin yada labarai na cikin gida sun ce adadin fasinjojin da suka jikkata ya haura 300.

Firaministan Indiya Narendra Modi ya nuna damuwa ainun kan lamarin.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here