Yadda aka tarbi uwar gidan shugaban kasa Remi Tinubu yayin da ta fara aiki a matsayin “First lady”

0
76

Misis Oluremi Tinubu, uwargidan shugaban kasa Bola Tinibu, a ranar Litinin a Abuja, ta karbi mukamin uwargidan shugaban kasar Najeriya.

Misis Tinubu da ta isa bangaren uwargidan shugaban kasa ta samu rakiyar mataimakan ta kan harkokin tsaro.

Uwargidan shugaban kasa a lokacin da ta isa wurin, ta samu tarba daga babban sakatare na fadar gwamnatin jihar, Mista Tijjani Umar da sauran shugabannin sassan ofishin uwargidan shugaban kasa.

A don haka aka jagoranci Misis Tinubu a rangadin wasu ofisoshi a bangaren uwargidan shugaban kasa, wadanda suka hada da bangaren gudanarwa, ICT, yada labarai, da sashin girke-girke.

An haifi Mrs Tinubu a ranar 21 ga Satumba, 1960, mahaifiyarta Itsekiri da kuma mahaifinta Bayarabe.

Ta yi Digiri na farko a fannin Ilimi a Jami’ar Ife kuma ta yi kwasa-kwasai da dama a wasu manyan makarantu.

Ta taba zama matar Gwamnan Jihar Legas a tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007 sannan aka zabe ta a matsayin Sanata mai wakiltar Legas ta tsakiya a Majalisar Dattawa.

Misis Tinubu ta aiwatar da ayyukan jin kai da dama domin rage wahalhalun da marasa galihu ke fuskanta a mazabarta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here