Tallafin mai: Kungiyoyin kwadago sun janye shiga yajin aiki bayan ganawa da gwamnati

0
74

Kungiyoyin kwadago da suka hada da kungiyar ma’aikata (NLC) da ta ‘yan kasuwa (TUC) sun dakatar da yajin aikin da suka shirya tsunduma a ranar Laraba, sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

Dakatar da yajin aikin ya biyo bayan wata ganawa da kungiyoyin suka yi da wakilan gwamnatin tarayya.

Kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ne ya jagoranci tawagar gwamnati inda ya bayyana wa kungiyoyin kudurin gwamnati akan shirinta na magance koken kungiyoyin.

A cewar kakakin majalisar, gwamnatin tarayya da TUC da kuma NLC za su kafa wani kwamitin hadin guiwa da zai duba shawarar duk wani bukatar karin albashi da kuma tsari da lokacin aiwatar da tsarin.

Ya ce, gwamnatin tarayya da TUC da kuma NLC za su sake duba tsarin musayar kudi da bankin duniya ke bayarwa tare da tabbatar da cewa an sanya masu karamin karfi a cikin shirin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here