A sassan ƙasar dai jama’a na ta bukukuwa domin nuna goyon bayansu ga juyin mulkin.
Hasali ma, rundunar tsaron ƙasar ta sanar da goyon bayanta ga shugaban rundunar tsaron fadar gwamnati kan juyin mulkin.
Sojojin dai sun soke zaɓen da Bongo ya lashe, tare da rushe masu riƙe da muƙaman siyasa kuma sun rufe iyakokin ƙasar, bayan juyin mulkin na ranar Laraba.
Idan juyin mulkin Gabon ya tabbata, zai zama na takwas da sojoji suka yi cikin shekara uku a nahiyar Afirka, kuma duk ƙasashen da Faransa ta raina a baya.