‘Yan Gabon sun yaba da juyin mulkin da sojoji suka yi

0
117
Gabon
Gabon

A sassan ƙasar dai jama’a na ta bukukuwa domin nuna goyon bayansu ga juyin mulkin.

Hasali ma, rundunar tsaron ƙasar ta sanar da goyon bayanta ga shugaban rundunar tsaron fadar gwamnati kan juyin mulkin.

Sojojin dai sun soke zaɓen da Bongo ya lashe, tare da rushe masu riƙe da muƙaman siyasa kuma sun rufe iyakokin ƙasar, bayan juyin mulkin na ranar Laraba.

Idan juyin mulkin Gabon ya tabbata, zai zama na takwas da sojoji suka yi cikin shekara uku a nahiyar Afirka, kuma duk ƙasashen da Faransa ta raina a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here