Zanga-zangar korar dakarun Faransa daga Nijar ta shiga rana ta uku

0
101

A jamhuriyar Nijar, ana sa ran ƙarin zanga-zanga a birnin Yamai game da neman dakarun Faransa su fice daga ƙasar ta yammacin Afirka.

A jiya Asabar dubban mutane suka yi gangami a wajen sansanin sojin Faransa da ke Yamai.

Akwai dakarun Faransa aƙalla 1,500 a Nijar waɗanda ke yaƙi da masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel.

Dangantaka tsakanin Nijar da tsohuwar uwargijiyarta ta ƙara tsami tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa Shugaba Mohamed Bazoum a watan Yuli da ya wuce.

A ranar Juma’a shugaban sojin Nijar ya soki matakin ƙin amincewa da gwamnatinsu da Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yi, yana mai cewa kullum suna magana da Bazoum ta wayar tarho.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here