Sarkin Zazzau ya yi wa mazauna garin sa gargadi

0
127

Sarkin Zazzau a Jihar Kaduna, Malam Ahmed Nuhu Bamalli, ya gargadi mazauna Masarautar musamman matasan Gwargwaje da su kaurace wa zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a yau Juma’a.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Aminiya ta rabawa manema labarai a Zariya.

Hakan ya biyo bayan tashin wutar lantarki da aka yi a yankin wanda ya yi sanadin kona wutar lantarkin kimanin mutane 11 tare da lalata dukiyoyi a unguwar Gwargwaje da ke Zariya a jihar Kaduna.

Sanarwar ta ce, “Wannan ba daidai ba ne. Abin takaici ne yadda wasu jiga-jigai/dattijai ke tursasa wa wadannan matasa wani abu da ka iya haifar da karya doka da oda a Gwargwaje da sauran wurare.

“Ina kira ga dukkan shugabannin wannan kungiya da su gargadi mutanen da ke karkashin su da su guji wannan abin da ba za a amince da shi ba.”

Bamalli ya yi nuni da cewa akwai hanyar farar hula ta nuna rashin jin dadi amma ba ta hanyar zanga-zanga ko tarzoma ba.

Sarkin ya yi gargadin cewa “’yan sanda da sauran jami’an tsaro sun shirya tsaf don hana duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya, yana mai gargadin a yi wa matasa jagora.”

Sarkin wanda ya ziyarci al’umma a baya da kuma jajantawa ya kuma jajanta wa iyalan da suka rasa ‘yan uwansu.

Ya kuma bukaci al’umma da su baiwa kamfanin wutar lantarki dama su zo su yi magana a kan hanyar da za a bi, maimakon tayar da tarzoma.