Babu wanda ya isa ya alakanta ni da satar dukiyar jama’a – Buhari

0
99

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce babu wanda zai alakanta shi da satar dukiyar jama’a a lokacin da yake kan mulki.

Buhari ya nuna cewa bai tara wata dukiya a boye ba, “Ba ni da ko taku daya na fili a kasar waje.”

Da yake magana a Damaturu, a Jihar Yobe a wajen liyafar da aka shirya domin karrama shi a daren ranar Litinin kamar yadda kakakinsa, Femi Adesina, ya sanar cikin wata sanarwar da ya fitar, ya nanata rantsuwar da ya yi na cewa zai yi gaskiya har ranar da zai kammala wa’adinsa na mulki.

Ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kasancewa masu kishin kasa, “Sama da shekara 30 ina fada, ba mu da wata kasa da ta wuce mana Nijeriya, ya kamata mu tsaya mu hada karfi da karfe mu ceto ta.’’

Shugaban ya nuna farin cikinsa kan yadda lamura ke kara dawowa daidai a jihohin Arewa Maso Gabas da suka sha fama da matsalar tsaro.