Ina aka kwana kan ceto ƴanmatan Chibok bayan shekara tara?

0
123

Shekara tara bayan sace ɗalibai mata kusan 300 daga makarantar sakandare ta Chibok, har yanzu babu labarin inda guda 96 suke.

A wata sanarwa da ƙungiyar Amnesty International ta fitar ranar Juma’a, a wani ɓangare na ranar tunawa da ranar da aka sace ɗaliban, ƙungiyar ta soki gwamnati bisa abin da ta kira ‘gaza kare su’.

A ranar 14 ga watan Afrilun shekara ta 2014, lokacin da rikicin Boko Haram ya yi ƙamari a yankin Arewa-maso-gabashin Najeriya, wasu mayaƙa suka kai farmaki a Makarantar Sakandare ta Chibok inda suka sace yara mata 276.

Daga baya sojoji sun samu nasarar ƙwato wasu daga cikin su, wasu kuma sun kuɓuta, yayin da ƙungiyar kuma ta sako wasu.

A sanarwar da ƙungiyar BBOG mai fafutikar ganin an ceto ɗaliban ta fitar domin tunawa da ranar, ta ce gazawar gwamnati wajen ceto yaran babban abin kunya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here