Shugaban kasa Tinubu zai shafe makonni 2 yana hutawa a Burtaniya

0
57

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kammala shirin ficewa daga kasar nan a yau laraba don shafe makonni yana hutawa a kasar Burtaniya.

Tafiyar ta kasance a can shugaban kasar zai yi hutun da yake tafiya a kowacce shekara.

Karanta karin wasu labaran:Wani mutum zai hallaka kansa saboda mulkin shugaba Tinubu

Mai taimakawa shugaban kasar na musamman a fannin yada yada labarai da tsare tsare Bayo Onanuga, ne yayi bayanin cewa shugaban zai yi amfani da hutun makonni biyun don yin duba akan wasu ayyukan da gwamnatin sa tayi cikin shekara daya, musamman sauye sauyen da ya yiwa fannin tattalin arzikin Nigeria.

Sanarwar tace Tinubu, zai dawo Nigeria, da zarar wa’adin kwanakin hutun sa ya kare.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here