Wata mata ta yi garkuwa da ‘yarta, ta bukaci mijinta ya biya fansar miliyan 3 a Kano

0
83

Wata mata mai shekarau 25 mai suna, Rahama Sulaiman, ta shiga hannun jami’an ‘yan sanda a Kano bisa zarginta da yin garkuwa da ‘yarta ‘yar shekara 6 mai suna Hafsat Kabiru tare da neman mijinta ya biya ta naira miliyan uku.

Matar dai ta kai yarinyar wurin wani dan uwanta da ke garin Madobi domin ya ajiye mata ita kan zata yi tafiyar kwana hudu.

Da yake magana a lokacin da yake gabatar da wanda ake zargin da sauran masu laifin a hedikwatar ‘yan sandan Kano, kwamishinan ‘yan sandan, Muhammad Usaini Gumel, ya ce sun samu rahoto daga mijin mai suna, Kabiru Shehu, cewa an yi garkuwa da ‘yarsa.

“A yayin wani bincike da aka gudanar, an kubutar da yarinyar a karamar hukumar Madobi.”

Da take magana da manema labarai bayan an kama ta, wadda ake zargin ta ce tsohon mijin nata bai ba ta kudin ciyar da yarant ba sama da watanni 10, don haka ta yanke shawarar yin hakan domin ta samu kudin kula da ‘ya’yansa.

“Na kira shi na ce masa ‘yarmu ta bace, muka je wurin ‘yan sanda tare muka kai rahoton lamarin. A cikin ofishin ‘yan sanda na ba shi lambar mutumin da zai karbi kudin fansa,” inji ta.

Ta ce ta yi nadamar abin da ta aikata kuma ta sanar da cewa ta sasanta da mijinta.

Mijin wanda ya tabbatar da cewa sun yi sulhu, ya kara da cewa matarsa ​​ba ta taba yin haka ba.

Rundunar ta kuma kama wasu masu laifin da suka hada da masu garkuwa da mutane da dillalan kwayoyi, sannan kuma sun kwato sama da 600 na tabar wiwi.

Sai dai kwamishinan ya ce za a gurfanar da duk wadanda ake zargin a gaban kotu bayan gudanar da bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here