Karya darajar Naira: Ɗangote ya faɗo daga mai kuɗin Afirka

0
117

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote ya faɗo daga matsayinsa na mai arzikin da yafi kowa kuɗi a nahiyar Afirka sanadiyyar karyewar darajar Naira.

Alhaji Aliko Ɗangote ya riƙe wannan kambin tsawon shekaru 12 amma yanzu ya koma na biyu, a cewar mujallar Forbes mai ƙididdige kuɗin masu arzikin duniya.

Ɗan kasuwar Afirka ta Kudu, Johannes Rupert shi ne ya maye gurbinsa a matsayin maikuɗin Afirka.

Rahoton da Forbes ta fitar a a ranar Lahadi yace Alhaji Aliko Ɗangote ya yi asarar fiye da $3.4 biliyan a rana guda sakamakon karyewar darajar Naira.

Sauran manyan masu kuɗin Najeriya su ma sun girgiza sakamakon karyewar Nairar.

Alhaji Abdulsamad Rabi’u, shugaban kamfanin BUA ya yi asarar $2.7 biliyan inda ya sauka daga matsayi na huɗu zuwa na shida a jerin masu kuɗin Afirka.

Babban Bankin Najeriya ne dai ya cire wa bankuna takunkumin cinikin Dalar Amurka, abin da ya haddasa faɗuwar darajar Naira.

Wannan ta sa a hukumance canjin ya kai N655/$1 saɓanin N471/$1 a farkon makon da ya gabata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here