HomeLabarai'Yan Najeriya miliyan 95 ne za su kada kuri'a a zaben 2023...

‘Yan Najeriya miliyan 95 ne za su kada kuri’a a zaben 2023 – INEC

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Wasu alkaluma da hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya (INEC) ta fitar, sun nuna cewa ‘yan kasar akalla mutum miliyan 95 ne za su kada kuri’a a zabukan shekarar 2023 da za su gudana a kasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu da ke bayyana hakan a jiya Laraba yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan tabbatar da gudanar da karbabbun zabuka a kasashe da ya gudana a birnin Washington na Amurka ya bada tabbacin shirye-shiryen hukumar da ya ke jagoranci na gudanar da sahihin zabe.

A cewar farfesa Yakubu yayinda jumullar kasashen yammacin Afrika 14 ke da yawan wadanda suka cancanci kada kuri’a miliyan 73, Najeriya da ke zama cikon ta 15, ne da yawan masu kada kuri’ar miliyan 95 ita kadai.

Wannan kididdiga ta zo ne a yayin da ya rage kasa da watanni biyar a gudanar da zaben shugabancin Najeriya a 2023, babban zabe na bakwai a jere tun bayan komawar kasar zuwa mulkin dimokaradiya a shekarar 1999.

 

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories