HomeLabarai‘Yan sanda sun damke wani matashi bisa zargin kashe mahaifinsa

‘Yan sanda sun damke wani matashi bisa zargin kashe mahaifinsa

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Rundunar ‘yansandan Jihar Legas ta damke wani matashi dan shekara 21, wanda ake zargin ya kashe mahaifinsa mai shekaru 70 a duniya.

Kakakin rundunar ‘yansandan, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN), a ranar Talata.

Hundeyin ya ce, rundunar ‘yansanda da ke yankin Abule-Egba a jihar ta samu rahoton kisan daga mahaifiyar wanda ake zargin a ranar Asabar.

Ya ce rahoton ya bayyana cewa da misalin karfe 3:40 na safiyar ranar Asabar, wanda ake zargin ya yi amfani da wani abu mai kaifi ya kashe mahaifinsa a dakinsa.

“Mai karar ya kara da cewa a lokacin da ya isa babban asibitin Oke-Odo, likita ya tabbatar da rasuwar marigayin.

“Yansanda sun ziyarci wurin da aka aikata laifin, sannan an kai gawar zuwa dakin ajiye gawa na babban asibitin Isolo domin kara bincike a kan ta.

“An kai wanda ake zargin zuwa sashen binciken kisan gilla na sashen binciken manyan laifuka na jihar, Panti, domin gudanar da bincike,” in ji shi.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories