HomeLabaraiJami’an tsaro sun kashe kasurgumin dan bindigar nan, Dogo maikasuwa a Kaduna

Jami’an tsaro sun kashe kasurgumin dan bindigar nan, Dogo maikasuwa a Kaduna

Date:

Related stories

Abba gida-gida ya lashe zaben gwamnan Kano

Hukumar Zabe ta Kasa, INEC ta sanar da cewa...

INEC na neman ta ce zaben gwamnan Kano ‘Inconclusive’ ne — Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, sanata Rabiu...

Zaben gwamnan Kano: Ratar kuri’ar da ke tsakanin NNPP da APC

Bayan bayyana sakamakon kananan hukumomi 44 na zaben gwamnan...

Jami’in tattara sakamakon zabe ya yanke jiki ya fadi a hedikwatar INEC a Kano

Jami’in tattara sakamakon zabe, Farfesa Muhammad Yushau na karamar...

Sakamakon zaben gwamnonin jihohin Najeriya

Wannan shafin zai rika kawo muku kammalallen sakamakon zaben...

Gwamnatin Jihar Kaduna ta tabbatar da kashe wani kwamandan ‘yan bindiga da aka fi sani da Dogo Maikasuwa a wani kazamin artabu da jami’an tsaro suka yi.

A wata sanarwa da kwamishinan ma’aikatar tsaron cikin gida, Samuel Aruwan, ya fitar a ranar Juma’a, ya ce Dogo Maikasuwa wanda aka fi sani da ‘Dogo Maimillion’ ya jagoranci hare-hare da sace-sacen jama’a da ke kan hanyar Kaduna zuwa Kachia da kuma kananan hukumomin Chikun da Kajuru a jihar.

Sanarwar ta bayyana Dogo a matsayin daya daga cikin ‘yan ta’adda mafi gawurta da ke jagorantar sauran al’umma wajen ta’addanci a jihar.

Aruwan ya kara da cewa, Dogo ya jagoranci ‘yan bindiga nasa wajen aikata ta’asa da muguwar dabi’a, inda sukan kashe wadanda aka yi garkuwa da su a lokacin da aka jinkirta kai musu kudin fansa.

Aruwan, ya ce sauran ‘yan bindigar sun tsere da raunukan bindiga.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories