HomeLabaraiAn kai wa kasar Poland hari

An kai wa kasar Poland hari

Date:

Related stories

INEC ta ayyana 29 ga Maris a matsayin ranar zaben cike gurbi a Adamawa

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta...

IPOB ta umarci ‘yan kabilar Igbo da ke Legas su koma gida

Kungiyar masu rajin kafa ‘yantacciyar kasar Biafara ta IPOB,...

Sarkin Kano ya taya Abba Kabir murnar lashe zaben gwamnan Kano

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero ya taya Abba Kabir...

Mata magoya bayan PDP na zanga-zangar kin amincewa da zabe a Kaduna

Wata tawagar mata sanye da bakaken kaya na jam’iyyar...

Gwamnatin Poland ta yi kira ga al’ummarta da su kwantar da hankalinsu,  bayan  da mutum biyu suka rasa rayukansu sanadin  fadawar wani makami mai linzami a wani kauye da ke kusa da kan iyakar kasar da Ukraine.

Shugaba Andrzej Duda ya ce makami ne da aka kera a Rasha amma babu cikakken bayani a kan wanda ya harba shi.

Shugaba Duda ya fada wa ‘yan jarida cewa : ”Ba mu da wata kwakkwarar shaida ya zuwa yanzu a kan wanda ya harbo makamin, akwai yuwar cewa makami ne  da aka kera a Rasha amma wani abu ne da ake gudanar da bincike a kansa a halin yanzu.”

Firaministan Poland Mateusz Morawiecki  ya ce gwamnati za ta tsaurara tsaro a sararin samaniyar kasar  sakamakon al’amarin da ya faru.

“ Mun yanke shawarar ganin cewa wasu daga cikin zababbun rundunoninmu na dakarun kasar  sun kasance cikin shirin ko-ta-kwana musamman a fannin da ya shafi sa ido a kan  sararin samaniya” a jawabin da ya yi wa ‘yan jarida.

Al’amarin wanda ya janyo damuwa tsakanin mambobin kungiyar tsaro ta Nato wanda Poland mamba ce a ciki ya janyo musayar kalamai tsakanin Kyiv da kuma Moscow.

Rasha ta bayyana ikirarin da ake yi a kan cewa ita ce ta ke da alhaki a matsayin takalar fada daga wurin Kyiv wadda manufarta ita ce ta ja sauran kasashen duniya a cikin rikici  dan a yi mata taron-dangi

Sai dai a daya bangaren Ukraine ta yi watsi da zargin na Rasha, a kan cewa ita ce take da alhakin harin a matsayin ba komai ba ne illa kutungwila ce kawai daga Rasha.

Ministan harkokin wajen Ukraine Dmytro Kuleba a shafinsa na Twitter ya ce: ”A yanzu Rasha ta gabatar da wani bayani da ya yi zargin cewa makamin  tsaron sararin samaniyar Ukraine ne ya fada a yankin Poland. Wannan kuma ba dai dai ba ne.

Subscribe

- Never miss a story with notifications

- Gain full access to our premium content

- Browse free from up to 5 devices at once

Latest stories